Yan bindiga sun yi garkuwa da tsohon dan majalissar dokokin jihar Ogun

Yan bindiga sun yi garkuwa da Maruf Musa tsohon mamba a majalisar dokokin jihar Ogun.

Musa wanda ya wakilci mazabar Ogun Waterside daga shekarar 2007 zuwa 2011 a majalisar jihar an yi garkuwa da shi ne a ranar Talata da daddare a Ibiade dake karamar hukumar Ogun Waterside.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun yi harbi domin tarwatsa mutane kafin suyi awon gaba da dan majalissar lokacin da ake yin Sallah a wani masallaci dake farfajiyar gidansa.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, Babaseyi Boluwatife ya tabbatarwa da jaridar The Cable faruwar lamarin.

Boluwatife ya ce tuni aka baza jami’an tsaro domin kubutar da shi.

Ya shawarci al’umma da su kwantar da hankalinsu kana su jira karin bayanai daga hukumomin tsaro.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]