’Yan Bindiga Sun Kona Mutane Hudu Da Ransu A Zamfara Bisa Zargin Kin Biyan Haraji

Akalla mutane hudu sun rasa rayukansu a daren ranar Alhamis bayan ’yan bindiga sun kai hari kauyen Gwargwaba da ke gundumar Nahuce a karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara.

Rahotanni sun nuna cewa ’yan bindigar, wadanda aka ce suna dauke da manyan makamai, sun mamaye kauyen da misalin karfe 6:00 na yamma tare da banka wa gidaje da dama wuta. Mutanen da suka mutu an ce wutar ta kama su ne a cikin gidajensu.

Baya ga haka, maharan sun lalata kayan abinci tare da kashewa da kuma kona dabbobin mutanen kauyen.

Wani masani kan sha’anin tsaro, Bakatsine, ya bayyana a wani sakon da ya wallafa a shafin X cewa harin ya biyo bayan kin amincewar mutanen kauyen na biyan harajin da ’yan bindigar suka kakaba musu.

A cewarsa, kin biyan harajin ne ya fusata ’yan bindigar, lamarin da ya haifar da wannan mummunan daukar fansa.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]