’Yan Bindiga Sun Kona Mutane Hudu Da Ransu A Zamfara Bisa Zargin Kin Biyan Haraji

Akalla mutane hudu sun rasa rayukansu a daren ranar Alhamis bayan ’yan bindiga sun kai hari kauyen Gwargwaba da ke gundumar Nahuce a karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara.

Rahotanni sun nuna cewa ’yan bindigar, wadanda aka ce suna dauke da manyan makamai, sun mamaye kauyen da misalin karfe 6:00 na yamma tare da banka wa gidaje da dama wuta. Mutanen da suka mutu an ce wutar ta kama su ne a cikin gidajensu.

Baya ga haka, maharan sun lalata kayan abinci tare da kashewa da kuma kona dabbobin mutanen kauyen.

Wani masani kan sha’anin tsaro, Bakatsine, ya bayyana a wani sakon da ya wallafa a shafin X cewa harin ya biyo bayan kin amincewar mutanen kauyen na biyan harajin da ’yan bindigar suka kakaba musu.

A cewarsa, kin biyan harajin ne ya fusata ’yan bindigar, lamarin da ya haifar da wannan mummunan daukar fansa.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]