Yan Bindiga Sun Halaka Mutane 6 Da Sace Wasu Mutane 13 A Jihar Zamfara – AREWA News


A cikin mutane hudu da yan bindigan suka halaka, uku daga cikin su raunin harbin bindiga ya yi sanadiya mutuwarsu inda yan bindigan suka yiwa dayan matashin yankan rago.
Haka kuma, ‘yan bindigan sun aukawa wata motar yakin sulke da ke kan hanyar zuwa kai dauki a garin na Dan Sadau da harbin bindiga kana suka kona motar, saidai matukin motar yakin ya sami tsira da ransa a yayin harin.

Motar Sulke Da Yan Bindiga suka kona a Zamfara.
Motar Sulke Da Yan Bindiga suka kona a Zamfara.

Wakilinmu a jihar ta Zamfara ya tabbatar mana da labarin hakan ne bayan halartar jana’izar mutane 4 da suka rasa ransu sakamakon harin na yan bindigar, da misalin karfe 10 da rabi na safiyar yau juma’a.
Mahukunta daga jihar ta Zamfara ma sun tabbatar da aukuwar lamarin ga wakilinmu, inda suka ce an fara aikin ceto mutanen da yan bindigan suka yi awon gaba da su.
A halin yanzu dai jami’an tsaro da suka hada da sojoji da ‘yan sanda sun isa wurin motar sulke da yan bindigan suka kona don janye ta daga kan hanya.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...