Yadda aka cinna wa ‘yar jam’iyyar PDP wuta a kogi

Kogi

Rahotanni sun nuna cewa wasu da ake zargin ‘yan dabar siyasa ne sun cinna wa wata shahararriyar ‘yar siyasa a Kogi wuta ranar Litinin.

Wasu jaridun Najeriya sun ruwaito cewa kakakin rundunar ‘yan sanda na jihar Kogi, William Aya ya bayyana cewa, Salome Abuh mai shekaru 60 wadda ita ce shugabar mata ta jam’iyyar PDP a mazabar Ochadamu a karamar hukumar Ofu, na barci a gidanta lokacin da ‘yan dabar suka cinna wa gidan wuta daf da magariba.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, William Aya ya fitar, ta ce al’amarin ya faru ne ranar Litinin da misalin karfe 4:30 na yamma.

Sanarwar ta ce wani mai suna Musa Efu daga garin Ochadamu a karamar hukumar Ofu ya kai korafi a ofishin ‘yan sanda cewa an samu rashin jituwa tsakanin wani dan jam’iyyar PDP da wani dan jam’iyyar APC inda dan jam’iyyar ta PDP ya daba wa dan APC wuka a cinya.

Mutumin da aka caka wa wukar dai ya mutu a kan hanyar zuwa asibiti.

Hakan ne ya harzuka matasan yankin suka dunguma zuwa gidan kawun mutumin da ya yi kisan inda suka kona gidan abin da ya yi sanadiyyar kone da kashe Salome Abuh mai shekara 60.

Matasan sun kuma kone wasu karin gidaje uku.

Rundunar ‘yan sanda ta ce tana ci gaba da bincike domin gano mutanen da ake zargi.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...