Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tabbatar da bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo, inda aka tabbatar da mutum ɗari da ɗaya sun kamu da cutar, yayin da mutum goma suka mutu.
Shugaban WHO, Tedros Ghebreyesus, ya bayyana cewa akwai sama da mutum ɗari tara da ake zargin sun kamu da cutar da kuma mutuwar mutum ɗari biyu da ashirin da ake zargi, lamarin da ya nuna cewa annobar ta fi yadda aka tabbatar a yanzu girma.
Ya ce rikice-rikice da matsalolin jin ƙai a wasu yankunan ƙasar na hana jami’an lafiya dakile yaduwar cutar cikin sauƙi.
WHO ta kuma ɗaga matakin barazanar cutar zuwa mafi muni saboda saurin yaɗuwarta da rashin ingantaccen rigakafi ko magani ga nau’in Bundibugyo na Ebola.
Tedros ya ce WHO na aiki tare da hukumomin DR Congo da Uganda domin ƙarfafa matakan dakile cutar, ciki har da gano waɗanda suka yi hulɗa da masu ɗauke da ita, samar da cibiyoyin jinya da wayar da kan jama’a.
A Uganda kuma, an tabbatar da ƙarin mutum biyu ma’aikatan lafiya sun kamu da Ebola, lamarin da ya kai jimillar masu cutar zuwa bakwai tare da mutum ɗaya da ya mutu.
Ministan Lafiya na DR Congo, Roger Kamba, ya ce matsalar tsaro da ƙarancin kayan gwaje-gwaje sun jinkirta matakan farko na yaƙi da cutar.
WHO Ta Tabbatar Da Mutane 101 Da Suka Kamu Da Ebola a DR Congo

