Cutar Korona : Mmutum miliyan biyu za su iya mutuwa saboda korona — WHO

Takunkumi

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce akwai yiwuwar cutar korona ta hallaka sama da mutane miliyan biyu, matsawar ba a samu hadin gwiwa tsakanin kasashen duniya don dakile ta ba.

Dama tuni mutum miliyan daya sun mutu, a kasashen da cutar ta yadu a duniya.

Daraktan agajin gaggawa na hukumar Michael Ryan, ya ce a halin yanzu, akwai yiwuwar karin mutum miliyan daya su mutu, la’akari da matakin cutar da ake kai a yanzu haka.

Amurka ce kasar da tafi fama da korona, kuma kawo yanzu ta hallaka fiye da mutum dubu dari biyu a can.

Yaya zan kare kaina daga cutar?

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce:

■ Ku wanke hannayenku da sabulun gargajiya ko sabulun ruwa da ake wanke hannu da shi, wato hand gel, wanda zai iya kashe kwayoyin cuta

■ Ku rufe hanci da bakinku lokacin da kuke yin atishawa da kyallen fyace majina – sannan ku wanke hannayenku bayan kun yi atishawa domin hana kwayoyin cutar yaduwa.

■ Ku guji taba idanunku, ko hanci ko bakinku- idan hannunku ya taba wurin da cutar ta shafa, za ta iya yaduwa zuwa sauran sassan jikinku.

■ Kada ku rika matsawa kusa da mutanen da ke yawan atishawa ko tari da masu fama da zazzabi – za su iya watsa cutar cikin iska ta yadda ku ma za ku iya kamuwa da ita. – akalla ku matsa nesa da su ta yadda tazarar da ke tsakanin ku za ta kai kafa uku.

Alamomin cutar coronavirus

Da alama tana farawa ne daga zazzabi, sannan sai mutum ya soma tari.

Bayan mako guda, mutum zai rika fuskantar yankewar numfashi.

Don haka ya kamata mutum ya je asibiti idan ya fuskanci irin wadannan alamomi.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...