Wata mata ta kashe mijinta mai lalurar shanyewar ɓarin jiki

Ana zargin wata mata mai suna Rahimat Salaum da kashe mijinta dake da lalurar shanyewar ɓarin jiki a yankin Pegi dake birnin tarayya Abuja.

SP Josephine Adeh mai magana da yawun rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja a cikin wata sanarwa ranar Talata ta ce jami’an ƴan sanda na ofishin rundunar dake Pegi ne suka kama matar a ranar Litinin.

A cewar Josephine matar na ƙoƙarin tserewa ne da kayan mijin nata kafin ƴan sanda suje su kamata.

“Bayan yi mata tambayoyi wacce ake zargin ta amsa laifin kashe mijinta bayan da suka yi faɗa a tsakaninsu. Daga bisani ta yiwa ƴan sanda jagora zuwa wani gini da ba a kammala ba inda ta jefar da gawar da aka ƙone.”a cewar sanarwar.

Rundunar ta ce ana cigaba da gudanar da binciken kan lamarin.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]