Wani ginin bene mai hawa uku da ake tsaka da ginawa ya ruguzo a can jihar Legas.
Oluwafemi Oke-Osanyinto, shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Legas LASEMA, shine ya tabbatar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.
Ya ce wani mutum da ba a gane kowaye ba ya makale a cikin baraguzai yayin da ake cigaba da aikin ceto shi.
” Yanzu haka wani babban mutum na karkashin baraguzai kuma jami’an kai daukin gaggawa sun fara aikin ceto shi,” ya ce.
Ya kara da cewa hukumar na aiki da dukkanin wasu kayan aiki da suke dasu wajen ganin ceto shi kuma za a karasa rushe ginin da zarar an kammala aikin ceton.