Wani ginin bene mai hawa uku ya rushe a Legas – AREWA News

Wani ginin bene mai hawa uku da ake tsaka da ginawa ya ruguzo a can jihar Legas.

Oluwafemi Oke-Osanyinto, shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Legas LASEMA, shine ya tabbatar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Ya ce wani mutum da ba a gane kowaye ba ya makale a cikin baraguzai yayin da ake cigaba da aikin ceto shi.

” Yanzu haka wani babban mutum na karkashin baraguzai kuma jami’an kai daukin gaggawa sun fara aikin ceto shi,” ya ce.

Ya kara da cewa hukumar na aiki da dukkanin wasu kayan aiki da suke dasu wajen ganin ceto shi kuma za a karasa rushe ginin da zarar an kammala aikin ceton.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...