An zakulo mutane 6 daga cikin baraguzan ginin bene da ya ruguzo a Lagos

Mutane 6 aka samu nasarar cetowa daga cikin baraguzan ginin wani bene da ya ruguzo a yankin Alakija dake ƙaramar hukumar Amuwo-Odofin ta jihar Lagos.

Gbenga Omotosho kwamishinan yaɗa labarai na jihar Lagos ne ya bayyana haka a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis.

” An samu ruguzowar bene mai hawa shida a wurin hawa da saukar motar bas  dake Alakija a unguwar Satellite Town, mutane shida aka ceto daga baraguzan ginin, ” ya ce .

Kwamishinan ya bayyana haka ne  a matsayin ƙarin haske na cigaban da aka samu tun bayan da aka samu labarin ruguzowar ginin da safiyar ranar Talata.

“Ana cigaba da neman sauran wasu mutanen, ma’aikatan aikin ceto su na wurin.”

Ginin na kasuwanci na ɗauke da ƙananan shagunan da dama ya ruguzo da safiyar ranar Alhamis.

Amma kuma hukumar kashe gobara ta jihar Lagos a wata sanarwar da ta fitar ta tabbatar da cewa an samu nasarar ceto mutane 10 da ransu daga cikin baraguzan ginin da su ka ji rauni daban-daban.

More from this stream

Recomended