Uzodimma ya lashe zaɓen gwamnan Imo da gagarumar rinjaye

Dantakarar jam’iyar APC kuma gwamna mai ci, Hope Uzodimma ya sake lashe zaɓen gwamnan da aka yi a ranar Asabar.

Uzodimma ya samu nasara ne da gagarumin rinjaye kamar yadda sakamakon da hukumar zaɓe ta INEC ta fitar ya nuna.

Gwamnan ya samu nasara da kuri’a 540,308 akan manyan abokanan takararsa na jam’iyar PDP da Labour Party.

Sakamakon ƙananan hukumomin jihar 27 da INEC ta bayyana ya nuna cewa gwamnan ya lashe zaɓen da a dukkanin kananan hukumomin.

Jam’iyar PDP ce tazo ta biyu a zaɓen da kuri’a 71,503 sai kuma jam’iyar Labour Party inda ɗan takararta Athan Achonu ya samu kuri’a 64,081.

More News

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...