Uba Sani Ya Lashe Tikitin APC Na Zaɓen Gwamnan Kaduna Na 2027



Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC domin zaɓen shekarar 2027 bayan ya samu ƙuri’un amincewa dubu ɗari huɗu da hamsin da tara da dari uku da casa’in da uku a zaɓen fidda gwani da aka gudanar ranar Alhamis.

Uba Sani wanda shi kaɗai ne ya tsaya takarar, ya samu cikakken goyon bayan wakilai da shugabannin jam’iyyar APC daga sassa daban-daban na jihar.

Shugaban kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani na APC a Kaduna, Hon. Hafiz Kawu, ya bayyana zaɓen a matsayin wanda aka gudanar cikin lumana da gaskiya.

Bayan tabbatar da shi a matsayin ɗan takara, Gwamna Uba Sani ya gode wa ‘ya’yan jam’iyyar da al’ummar Kaduna bisa amincewar da suka nuna masa.

Ya ce gwamnatinsa ta samu nasarori a fannoni da suka haɗa da tsaro, zaman lafiya, ilimi da ayyukan raya ƙasa, tare da alƙawarin ci gaba da ƙarfafa haɗin kai da ci gaban jihar kafin zaɓen 2027.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]