Tsagin Wike sun kwace ikon   sakatariyar jam’iyar PDP

Rikicin da ya dabaibaye jam’iyar PDP ya dauki wani sabon salo a ranar lokacin da wani tsagin jam’iyar dake biyayya ga tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike su ka kwace ikon  ginin hedkwatar jam’iyar dake Wadata Plaza a Abuja.

Ana  tsaka da rikicin ne ɓangaren Wike ya nada, Muhammad Abdulrahaman a matsayin shugaban jam’iyar na riko bayan da suka dakatar da shugaban jam’iyar, Umar Damagum.

Tun da farko kafin a kawo halin da ake ciki yanzu sai da shugabancin jam’iyar karkashin jagorancin, Damagum ya dakatar da Samuel Anyanwu da kuma wasu shugabannin jam’iyar dake biyayya ga Wike.

Da yake wa yan jaridu jawabi a Abuja sabon shugaban jam’iyar ta PDP tsagin Wike ya ce kudirinsa shi ne haɗakan jam’iyar.

Shugaban ya gudanar da wata ganawa a hedkwatar jam’iyar tare da Anyanwu da kuma wasu shugabanni da suka fito daga tsagin na Wike.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]