Tsagin Wike sun kwace ikon   sakatariyar jam’iyar PDP

Rikicin da ya dabaibaye jam’iyar PDP ya dauki wani sabon salo a ranar lokacin da wani tsagin jam’iyar dake biyayya ga tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike su ka kwace ikon  ginin hedkwatar jam’iyar dake Wadata Plaza a Abuja.

Ana  tsaka da rikicin ne ɓangaren Wike ya nada, Muhammad Abdulrahaman a matsayin shugaban jam’iyar na riko bayan da suka dakatar da shugaban jam’iyar, Umar Damagum.

Tun da farko kafin a kawo halin da ake ciki yanzu sai da shugabancin jam’iyar karkashin jagorancin, Damagum ya dakatar da Samuel Anyanwu da kuma wasu shugabannin jam’iyar dake biyayya ga Wike.

Da yake wa yan jaridu jawabi a Abuja sabon shugaban jam’iyar ta PDP tsagin Wike ya ce kudirinsa shi ne haɗakan jam’iyar.

Shugaban ya gudanar da wata ganawa a hedkwatar jam’iyar tare da Anyanwu da kuma wasu shugabanni da suka fito daga tsagin na Wike.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]