Tirƙashi: Ƴan sandan Jigawa sun yi babban kamu

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa sun kama wasu mutane biyu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne.

Mataimakin jami’in hulda da jama’a na rundunar, ASP Abubakar Isah, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Dutse, babban birnin jihar.

Ya ce an kama wadanda ake zargin ne a ranar 12 ga Disambar 2023, a jihar Kano.

Ya bayyana sunayen wadanda ake zargin a matsayin Yusuf Yusuf dan shekara 25 daga unguwar Katoge da ke karamar hukumar Kazaure da kuma Umar Abubakar mai shekaru 23 daga kauyen Dakayyawa a karamar hukumar Kaugama.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]