Tirƙashi: Ƴan sandan Jigawa sun yi babban kamu

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa sun kama wasu mutane biyu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne.

Mataimakin jami’in hulda da jama’a na rundunar, ASP Abubakar Isah, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Dutse, babban birnin jihar.

Ya ce an kama wadanda ake zargin ne a ranar 12 ga Disambar 2023, a jihar Kano.

Ya bayyana sunayen wadanda ake zargin a matsayin Yusuf Yusuf dan shekara 25 daga unguwar Katoge da ke karamar hukumar Kazaure da kuma Umar Abubakar mai shekaru 23 daga kauyen Dakayyawa a karamar hukumar Kaugama.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...