Shugaban Najeriya mai ci a yanzu, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar a babban zaɓen shekarar 2027.
Rahotanni sun nuna cewa an sayi fom ɗin shiga takarar a madadinsa a ranar Talata a Abuja kan kuɗi naira miliyan 100.
Ɗan majalisa mai wakiltar Ikeja a majalisar Tarayya, James Faleke, ne ya sayi fom ɗin, inda yake daga cikin jagororin ƙungiyoyin da ke goyon bayan Tinubu.
A wani ɓangare kuma, sakataren tsare-tsare na jam’iyyar APC, Suleiman Argungu, shi ne ya miƙa fom ɗin bayan ƙaddamar da fara sayar da fom ɗin ga masu sha’awar tsayawa takara a jam’iyyar.
Tinubu Ya Sayi Fom ɗin Nuna Sha’awar Tsayawa Takarar Shugabancin Najeriya A 2027

