
Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya aike da sunan, Joseph Olasukanmi Tegbe a matsayin wanda zai naɗa sabon ministan wutar lantarki.
Mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga shi ne ya bayyana haka a ranar Alhamis.
Ya ce an mika sunansa ga majalisar dattawa domin tantancewa da kuma tabbatar da shi kamar yadda tsarin mulki ya tanada
Nadin nasa na zuwa ne biyo bayan ajiye aiki da tsohon ministan ma’aikatar, Adebayo Adelabu ya yi wanda ya tsaya takarar gwamnan jihar Oyo.
Tegbe ya yi fito ne daga jihar ta Oyo ya kuma samu gogewa a fannin aikin gwamnati da na kamfanoni masu zaman kansu.

