Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin Adewale Adeniyi a matsayin babban Kwanturolan Hukumar Kwastam ta Najeriya.
Daraktan yada labarai ga sakataren gwamnatin tarayya Willie Bassey ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.
A cewar sanarwar, nadin zai fara aiki ne daga ranar 19 ga Oktoba, 2023, kuma wa’adinsa ya biyo bayan wasu tanadin dokokin ma’aikatan gwamnati (PSR).
Idan ba a manta ba, a watan Yuni ne Tinubu ya nada Adeniyi a matsayin Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS) don maye gurbin tsohon CG, Hammed Ali.