Tinubu ya amince da naɗin sabon shugaban kwastom

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin Adewale Adeniyi a matsayin babban Kwanturolan Hukumar Kwastam ta Najeriya.

Daraktan yada labarai ga sakataren gwamnatin tarayya Willie Bassey ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

A cewar sanarwar, nadin zai fara aiki ne daga ranar 19 ga Oktoba, 2023, kuma wa’adinsa ya biyo bayan wasu tanadin dokokin ma’aikatan gwamnati (PSR).

Idan ba a manta ba, a watan Yuni ne Tinubu ya nada Adeniyi a matsayin Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS) don maye gurbin tsohon CG, Hammed Ali.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]