Sojoji Sun Ceto Dalibai Da Malamai 10 Daga Hannun ISWAP A Borno


Rundunar Operation Hadin Kai ta sanar da ceto ɗalibai da malamai 10 da mayaƙan ISWAP suka sace bayan harin da suka kai makarantar sakandaren fasaha ta Lassa a ƙaramar hukumar Askira/Uba ta jihar Borno.

A cewar rundunar, harin ya faru ne yayin da ɗalibai ke rubuta jarabawar NECO, inda nan take aka tura sojoji da jiragen yaƙi domin gudanar da aikin ceto.

Sanarwar ta ce bayan artabu da mayaƙan a yankin Daggu, sojojin sun ceto mutanen ba tare da sun ji rauni ba. Haka kuma an kashe wasu daga cikin mayaƙan tare da ƙwace babura bakwai da suka yi amfani da su wajen harin.

Sai dai rundunar ta tabbatar da mutuwar wani soja da kuma jami’in sa kai na JTF yayin musayar wuta.

Rundunar ta ƙara da cewa ana ci gaba da ƙoƙarin ceto sauran mutanen da aka sace tare da kamo waɗanda suka kai harin.

More from this stream

Recomended