Sojoji a Zamfara sun kashe yan bindiga 10 tare da kuɓutar da mutane 6

Sojojin rundunar Operation Hadarin Daji sun kashe akalla mutane 10 da ake zargin yan bindiga ne a jihar Zamfara.

A cewar Zagazola Makama wanda yake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya ce an kashe yan bindigar ne a wani harin kwanton ɓauna da sojoji suka maisu a yankin Gadan Zaima zuwa Dan Marke dake karamar hukumar Bukuyyum a ranar Talata.

Wasu majiyar sojoji ta bayyana cewa biyo bayan musayar wuta sojojin sun kuma samu nasarar kuɓutar da wasu mutane da aka yi garkuwa da su a wani daji dake iyakar Mahuta da Zuru a jihar Kebbi.

Majiyar ta ce yayin da aka samu nasarar kashe wasu daga cikin an kuma samu nasarar kama wasu.

Makama ya kara da cewa bingogi shida kirar AK-47, bindigar GPMG kudi naira miliyan 1 da kuma tabar wiwi aka gano a wurin yan bindigar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]