An kama wani mutum a Adamawa da ake zargi da yanka wata mata a Otal

A jihar Adamawa ana zargin wani mutum da yanka wuyan wata mata da kawo yanzu ba a bayyana sunanta ba.

Lamarin ya faru ne  tsakar a ranar Juma’a a Otal din Novex dake ƙaramar hukumar Girei ta jihar inda mutumin suka kama tare da matar.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa an ji karar ana  faɗa a cikin dakin da mutumin suka kama hakan ya sa aka je a duba halin da ake ciki kawai sai aka tarar da matar kwance cikin jini an yanka mata wuya,

Tuni aka dauke gawarta tare da ajiye ta a wani asibiti da ba a bayyana ba a yayin da jami’an ƴan sanda suka tsare wanda ake zargin.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin mai magana da yawun rundunar yana sandan jihar Adamawa,SP Suleiman Nguroje yace rundunar ta kama wani mutum guda da ake zargi da aikata laifin

Nguroje ya ce tuni rundunar ta dukufa wajen gudanar da bincike domin gano abin da ya faru kana ya yi kira da jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...