Rundunar Operation FANSAN YAMMA ta ce ta fara aikin haɗin gwiwa domin ceto shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu ta Jihar Zamfara, Nura Umar Abdullahi, bayan ƴan bindiga sun sace shi daga gidansa.
Rundunar ta bayyana cewa dakarunta sun ceto mutum 5 daga cikin iyalansa bayan sun yi musayar wuta da maharan, amma maharan sun tsere da shugaban ƙaramar hukumar zuwa cikin daji.
Sanarwar ta kuma tabbatar da mutuwar jami’an tsaronsa 3, da suka haɗa da ƴan sanda 2 da ɗan sintiri 1. Haka kuma, wani farar hula ya rasu yayin da wani mutum ya samu raunuka.
Rundunar ta ce tana ci gaba da haɗin gwiwa da ƴan sanda da DSS da kuma ƴan sa-kai domin gano maboyar maharan da kuma kuɓutar da shugaban ƙaramar hukumar cikin ƙoshin lafiya.
Sojoji Sun Fara Neman Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu Da Aka Sace

