Shin Da Gaske Jirgin Yakin Najeriya Ya Kashe Sojojin Kasar Bisa Kuskure? – AREWA News

VOA Hausa

Rahotanni daga Najeriya na cewa wani jirgin yakin saman Najeriya ya kashe wasu dakarun kasar bisa kuskure a yankin Mainok na jihar Borno da ke arewacin kasar.
Dakarun saman na taimakawa takwarorin aikinsu na kasa ne a yakin da Najeriya ke yi da mayakan Boko Haram da na ISWAP.
Wasu rahotanni sun ce adadin sojojin da aka kashe a wannan hari ya kai 30.
Sai dai rundunar sojin saman Najeriyar, ta fitar da wata sanarwa a ranar Litinin a shafinta na Twitter.
Ta ce ita ma ta ga rahotannin da wani bidiyo da yake ta yawo a shafukan sada zumunta da ke nuna harin da aka kai bisa kuskure, inda ta ce, tana kan bincike kan sahihancinsa.
“An ja hankalin rundunar sojin Najeriya, inda rahotanni ke cewa “yadda rundunar sojin saman Najeriya ta kashe sojoji 20 bisa kuskure a wani harin sama” a Mainok da ke da tazarar tafiyar kilomita 55 daga Maidguri.” Sanarwar ta Twitter ta ce.
Ta kara da cewa, “rundunar sojin saman Najeriya (NAF) na gudanar da bincike kan hoton bidiyo da rahotanni da ke ta yawo, kuma za a sanar da jama’a sakamakon binciken da zarar an kammala.”
A watan Janairun shekarar 2017, wani jirgin yakin sama na Najeriya ya kashe fararen hula sama da 100 a garin Rann da ke jihar Borno.
Lamarin ya faru ne bayan da jirgin yakin ya saki bama-bamai akan wani sansanin ‘yan gudun hijira bisa kuskure.
A ‘yan kwanakin nan, mayakan ISWAP da Boko Haram, sun yi ta kai hari a yankunan jihar Borno da Yobe.
Hakan ya sa jama’a da dama tserewa daga yankunan domin tsira da rayukansu.
Wasu rahotannin sun ce garin Geidam yanzu haka yana hannun kungiyar Boko Haram.
Yayin wani taron manema labarai da ya yi, Gwamnan Yobe Mai Mala Buni, ya bayyana irin mawuyacin halin da mayakan suka jefa garin na Geidam da suke ta kai wa hari tun daga ranar Juma’a.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...