Satar ‘Yan Matan Chibok Ta Shiga Shekara Ta Shida

Kimanin shekaru shida kenan da aka sace ‘yan matan a garin Chibok da ke arewa maso gabashin Najeriya a wani samame da ‘yan ta’addan Boko Haram suka kai a makarantar sakandaren a shekarar 2014 kana suka yi awon gaba da ‘yan mata 220.

A cikin shekarar 2017 ne hukumomin Najeriya suka karbo wasu a cikin ‘yan mata a wata musayar da gwamnatin ita ma ta saki wasu ‘yan kungiyar Boko Haram.

Ya zuwa yanzu akwai ‘yan mata da suka kai 112 da suka rage a hannun ‘yan ta’addan ba tare da sanin makomarsu ba.

Mrs. Rebecca Samuel mahaifiyar daya a cikin ‘yan matan da suka rage hannun ‘yan Boko Haram ta yi kira ga shugaban kasa da ya kara azama a kokarin kubutar da ‘yan matan.

Ta kara da cewa tana sane da kokarin da hukumomin gwamnati ke yi a kan wannan batu akwai bukatar kara kaimi.

Rebecca ta ce tana fuskantar kunci a rayuwarta da yawan tunani na rashin ‘yarta amma ta ce tana addu’a duk lokacin da za ta shiga bacci.

Mrs. Rebecca Samuel ta yi wadannan kiraye kirayen ne a wata hira da ta yi wakilin Sashen Hausa na Muryar Amurka a Abuja, Sale Shehu Ashaka.

Hukumomin Najeriya dai a baya, sun sha fadin cewa suna iya bakin kokarisu wajen ganin sun kubutar da ‘yan matan da suka rage.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...