Sojoji sun sake kuɓutar da wata daga cikin ƴan matan Chibok

Sojojin bataliya ta 81 na rundunar Operation Hadin Kai sun ceto daya daga cikin yan matan Chibok da aka yi garkuwa da ita a shekarar 2014.

A cikin watan Afirilun shekarar 2014 ne mayakan kungiyar Boko Haram suka sace yan matan su 276 daga makarantar sakandaren yan matan dake Chibok.

Tuni aka ceto da yawa daga cikin yan matan.

Yarinyar da aka ceto mai suna Mary Nkeki an gano ta ne a ranar 25 ga watan Agusta a karamar hukumar Dikwa dake jihar Borno.

Da yake magana a ranar Litinin a yayin mika ta ga gwamnatin jihar Borno, kwamandan rundunar, Gold Chibuisi ya ce an tilastawa Nkeki auren daya daga cikin yan kungiyar ta Boko Haram bayan da aka sace su tare da yan uwanta.

Da take magana kan halin da ta samu kanta a ciki a lokacin da take hannun yan ta’addar, Nkeki ta ce zama da yan ta’addar cike yake da wahala.

Nkeki ta ce ta tsere tare da mijinta da daddare daga sansanin yan ta’addar inda suka ci karo da sojojin dake sintiri.

Ta kara da cewa ta bar yan matan Chibok biyu a sansanin.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...