Tsohon Shugaban Najeriya Goodluck Ebele Jonathan ya ce zargin da tsohon Firaministan Birtaniya David Cameron ya yi masa na cewa shi ne ya hana ceto ‘yan matan Chibok “zuki ta malle ne kawai”.
David Cameron, wanda shi ne Firaministan Birtaniya a lokacin da abin ya faru, ya yi zargin cewa Shugaba Goodluck Jonathan ne ya kawo wa gwamnatin Birtaniya tsaiko wajen ceto ‘yan matan a lokacin da yake shugaban Najeriya.
Cameron ya yi zargin ne a wani littafi da ya wallafa mai suna For The Record.
Ya ce: “Mun hango ‘yan matan na Chibok daga sama a wani kasurgumin daji….amma da alama Shugaban Najeriya (na lokacin) Goodluck Jonathan likimo yake yi kuma a karshe da ya farka sai ya zargi kungiyar rajin ceto ‘yan matan da laifin siyasantar da al’amarin.
“Duk da irin muhimmancin abin, da muka bukaci mu ceto su sai ya ki yarda.”
Wannan zargin na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan matan na Chibok ke cika kwana 2,000 da sacewa.
A martanin da ya mayar wa Mista Cameron a shafinsa na Facebook, Goodluck Jonathan ya ce ya yi mamaki matuka kan kalaman nasa, kuma ya ce ya tabbatar da cewa ba shi kadai ne yake jin cewa Cameron ya sharara karya ba.
“Ba zan zama mutum na farko ba da yake kallon wadannan kalamai a matsayin zancen kawai, sannan kuma ganin yadda mutane suke yin martani a Birtaniya ma tabbas ba zan zama na karshe ba,” in ji Jonathan.
Ya kara da cewa: “Abin takaici ne Mista Cameron ya rika fadar irin wadannan abubuwa saboda duk cikinsu babu wanda ya faru.
“A matsayina na shugaban Najeriya, na rubuta wa David Cameron wasika da Barrack Obama na Amurka da kuma shugaban Faransa François Hollande har ma da na Ira’ila Benjamin Netanyahu duka domin nerman taimakonsu wajen ceto ‘yan matan nan.
“Ta yaya zan nemi a taimaka mani sannan kuma na ki karbar taimakon?”
Jonathan ya kuma ce tarihi ma ya karyata Mista Cameron domin kuwa lokacin da yana Shugaban Najeriya shi ne da hannunsa ya bai wa sojojin Birtaniya damar shiga jihar Sokoto domin ceto wasu ‘yan Birtaniyar da aka sace a watan Maris na 2012.