Sanata Goje ya bi sawun Pantami inda ya  yi watsi da tsarin maslaha da  aka bi wajen  fitar  da yan takara a Gombe

Sanata Danjuma Goje dake wakiltar mazaɓar tsakiyar jihar Gombe ya yi watsi da matakin maslaha da aka bi wajen fitar da ɗantakara da jam’iyar APC ta yi a Gombe

A ranar Lahadi ne dai masu ruwa da tsaki na jam’iyar ta APC ƙarƙashin jagorancin gwamnan jihar, Muhammad Inuwa Yahaya su ka ayyana sunan, DCP Muhammad Ahmadu Deba a matsayin ɗantakarar maslaha da aka fitar wanda zai gaji kujerar Goje

Amma kuma a wata sanarwa da mai taimaka masa, Sa’idu Muazu Kumo ya fitar, Sanata Goje wanda yake neman a sake zaɓensa a karo ya ce taron sulhu da ake ikirarin anyi gwamna Yahaya ne da wasu mutane  ƙalilan na yan takara  “ba a haɗa da dukkanin mutanen da aka tabbatar suna takara a jam’iyar APC na .”

A cewarsa,  dokar zaɓe ta bayyana a fili ƙarara halastattun hanyoyi biyu na yadda jamiyar siyasa za ta tsayar da dantakara ta kuma mikawa hukumar zabe gabanin zaɓen 2027.

Ya ce dole ne abi waɗannan kaidoji domin a tabbatar da anyi adalci.

Ya kara da cewa a mazabu da dama mutane sun sayi fom din takara amma ba a  yi zaman fitar da yan takarar da su ba.

A ƙarshe ya yi kira da ayi zaɓen kai tsaye kamar yadda dokar zaɓen ta tanada ayi hakan idan aka gaza samun matsaya a tsakanin ƴan takarkaru.

More from this stream

Recomended