
Sanata Danjuma Goje dake wakiltar mazaɓar tsakiyar jihar Gombe ya yi watsi da matakin maslaha da aka bi wajen fitar da ɗantakara da jam’iyar APC ta yi a Gombe
A ranar Lahadi ne dai masu ruwa da tsaki na jam’iyar ta APC ƙarƙashin jagorancin gwamnan jihar, Muhammad Inuwa Yahaya su ka ayyana sunan, DCP Muhammad Ahmadu Deba a matsayin ɗantakarar maslaha da aka fitar wanda zai gaji kujerar Goje
Amma kuma a wata sanarwa da mai taimaka masa, Sa’idu Muazu Kumo ya fitar, Sanata Goje wanda yake neman a sake zaɓensa a karo ya ce taron sulhu da ake ikirarin anyi gwamna Yahaya ne da wasu mutane ƙalilan na yan takara “ba a haɗa da dukkanin mutanen da aka tabbatar suna takara a jam’iyar APC na .”
A cewarsa, dokar zaɓe ta bayyana a fili ƙarara halastattun hanyoyi biyu na yadda jamiyar siyasa za ta tsayar da dantakara ta kuma mikawa hukumar zabe gabanin zaɓen 2027.
Ya ce dole ne abi waɗannan kaidoji domin a tabbatar da anyi adalci.
Ya kara da cewa a mazabu da dama mutane sun sayi fom din takara amma ba a yi zaman fitar da yan takarar da su ba.
A ƙarshe ya yi kira da ayi zaɓen kai tsaye kamar yadda dokar zaɓen ta tanada ayi hakan idan aka gaza samun matsaya a tsakanin ƴan takarkaru.

