Ronaldo zai lashe kyautar takalmin zinare a Euro 2020

Cristiano Ronaldo

Asalin hoton, Getty Images

Watakila Cristiano Ronaldo ya lashe kyautar takalmin zinare a gasar cin kofin nahiyar Turai ta Euro 2020 a matakin wanda ya fi cin kwallaye a wasannin.

Koda yake an yi waje da Portugal mai rike da kofin a karawar zagaye na biyu, bayan da Belgium ta doke ta da ci 1-0 ranar 27 ga watan Yunin 2021.

Dan wasan Juventus ya ci Hungary kwallo biyu da Faransa da itama ya ci biyu da kuma Jamus da ya zura daya a raga,. jumulla guda biyar a karawar cikin rukuni kenan.

Dan kwallon Jamhuriyar Czech, Patrik Schick shima yana da biyar a raga a Euro 2020, sai dai Ronaldo na gabansa kasancewar ya bai wa Diogo Jota kwallo ya zura a ragar Jamus.

Kawo yanzu kamar yadda aka fitar da Ronaldo daga gasar bana, haka shima Schick ya yi ban kwana da wasannin Euro 2020.

Akwai ‘yan wasan da suka ci kwallo hur hudu da suka hada da Romelu Lukaku na Belgium da Karim Benzema na Faransa da dan wasan Sweden Emil Forsberg, wadanda sun dade da komawa gida.

Gasar ta bana ta kai karawar daf da karshe, kuma ‘yan kwallo uku ne suka zura uku-uku a raga da suka kai wasan daf da karshen da suka hada da Raheem Sterling na Ingila da kuma Harry Kane da Kasper Dolberg na tawagar Belgium.

Hakan dama ce da wani daga cikin ‘yan wasan nan su kamo Ronaldo, ko su haura shi a yawan cin kwallo a gasar bana, tunda wani ko wasu daga ciki sai sun kai karawar karshe.

Ranar Talata za a buga wasan daf da karshe tsakanin Italiya da Sifaniya, sannan ranar Lahadi a kece raini tsakanin Ingila da Denmark duk a Wembley.

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuÉ—aÉ—e

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...