
Shugaban kwamitin amintattu na jam’iyar adawa ta PDP, Adolphus Wabara ya yi kira ga hukumar zabe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC da ta amince da shugabannin riko na jam’iyar na kasa da kwamitin ya naɗa.
Wabara ya sanar da cewa a yanzu kwamitin amintattu ne keda iko da shugabancin jam’iyar sakamakon hukuncin kotun
A ranar Litinin ne tsagin na jam’iyar PDP dake samun goyon bayan gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde su ka naɗa ,Kabiru. Taninu a matsayin sabon shugaban riƙo na jam’iyar.
Sauran Mambobin da aka zaba sun haɗa Woyengikuro Daniel, Hamza Koshe, Ihediwa Nnabugwu, Isa Abubakar, Okechukwu Daniel, Theophilus Shan, Ini Ememobong, Aribisala Idowu, Bara’u Shafi’i, Ogbu Chinenyenwa, Umar Aji, da kuma Arapaja Taofeek.
Makon da ya gabata ne kotun ƙolin ta soke babban taron zaɓen shugabanni da PDP ta yi a birnin Ibadan na jihar Oyo inda anan ne aka zaɓi, Turaki tare da sauran shugabannin jam’iyar na kasa.
Kotun ta yanke hukuncin cewa ɗaukaka ƙarar da tsagin Turaki su ka yi bashi da tushe bare makama.
Amma kuma a wani martanin gaggawa da su ka fitar shugabancin jam’iyar PDP tsagin, ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike sun yi watsi da matakin inda su ka ce duk wani mataki da aka dauka ba za su amince da shi ba .

