Tsagin jam’iyyar PDP karkashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki ya ayyana tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Ebele Jonathan, a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a babban zaɓen shekarar 2027.
Jam’iyyar ta sanar da hakan ne bayan fitar da takardar shaidar tsayawa takarar Jonathan, yayin da Mataimakiyar Sakataren Yaɗa Labarai ta ƙasa na ɓangaren, Farida Umar, ta tabbatar da matakin.
Matakin ya fito ne bayan taron ƙasa na jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, inda aka sauya wurin taron cikin gaggawa bayan da ‘yan sanda suka hana mambobin jam’iyyar shiga wurin da aka fara tanada.
A yayin taron, mahalarta sun amince da tsayar da Jonathan takara, inda aka ce ya samu goyon bayan manyan jiga-jigan tsagin Turaki na jam’iyyar domin fafatawa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027.
Tsagin PDP Na Turaki Ya Tsayar Da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

