
Jam’iyar PDP ƙarƙashin jagorancin, Kabiru Tanimu Turaki ta ce ta ƙulla ƙawance da jam’iyar APM.
Da yake magana da jaridar The Cable a ranar Laraba, Ini Ememobong mai magana da yawun jam’iyar PDP ya ce an ƙulla ƙawancen ne biyo bayan taron shugabannin jam’iyyun adawa da aka gudanar a birnin Ibadan na jihar Oyo a watan Afrilu.
“karin wani ƙawancen na zuwa nan gaba, amma yanzu mun fara da wannan, ” a cewar Ememobong.
A watan da ya wuce ne jam’iyun adawa ciki har da PDP ɓangaren Turaki da ADC da kuma wani tsagi na jam’iyar NNPP suka sanar da shirin su na tsayar da dantakara guda a zaɓen shugaban ƙasa.
A ranar 7 ga wata ne gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed ya sayi fom din takarar sanata a jam’iyar APM kwanaki biyar bayan da ya fice daga jam’iyar PDP.
A jihar Oyo tuni ake ta raɗe-raɗin cewa gwamnan jihar, Seyi Makinde ya shirya komawa jam’iyar ta APM a lokacin wani taron gangamin siyasa da aka shirya gudanarwa a ranar Alhamis.
Gabanin komawarsa jam’iyar tuni wasu daga cikin ƴan majalisar dokokin jihar da kuma ta tarayya daga jihar ta Oyo suka sanar da komawarsu jam’iyar APM.

