
Sanata mai wakiltar mazaɓar, Bauchi ta tsakiya, Abdul Ahmad Ningi ya sanar da ficewarsa daga jam’iyar PDP.
Ningi ya bayyana haka a cikin wata wasikar yin murabus daga jam’iyar da ya aikawa da shugaban PDP na mazaɓarsa ta Ningi dake karamar hukumar Ningi ta jihar Bauchi.
A cewarsa ɗaukar matakin ya zame masa dole bayan tuntubar masu ruwa da tsaki makusantansa da kuma magoya baya.
Ningi ya shafe sama da shekaru 20 a cikin jam’iyar PDP.
Ya shiga jam’iyar ne a shekarar 1998 ta inda ya zama dan majalisar wakilai ta tarayya har sau biyu da kuma zama sanata har sau biyu duk a ƙarƙashin
A cewarsa rikicin cikin gida, rabe-rabe da kuma fifita bukatun wasu bangarori na daga cikin abubuwan dake raunata haɗin kan jam’iyar.
Ningi ya bayyana matakin barin jami’iyar PDP a matsayin wani mawuyacin lokaci a rayuwarsa ta siyasa.
Ya godewa jam’iyar PDP da kuma magoya bayansa kan damar da su ka ba shi.

