NDLEA ta kama wasu makafi uku dake kasuwancin miyagun ƙwayoyi

Hukumar NDLEA dake yaki da sha da hana fataucin miyagun kwayoyi ta kama wasu makafi uku dake gudanar da kasuwancin miyagun ƙwayoyi a tsakanin jihohin Kano da Lagos.

Mai magana da yawun hukumar Femi Babafemi shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa.

“Jami’an NDLEA sun kama wasu makafi uku waÉ—anda suke kasuwancin miyagun Æ™wayoyi a tsakanin Lagos da Kano a yayin da É—aya makahon na huÉ—u har yanzu ba aka kama shi ba,” a cewar sanarwar.

“Asirinsu ya tonu ne biyo bayan kama wani makaho da ake zargi mai suna Adamu Hassan É—an shekara 40 akan titin Gwagalada a Abuja akan hanyarsa ta zuwa Kano inda yake É—auke da abun mayen da ake kira skunk mai nauyin kilogram 12 a ranar 28 ga watan Oktoba.”

“Binciken da aka gudanar ya nuna cewa bai ma san abun da yake cikin jakar da aka ba shi ya kai Kano ba.”

Bayan cigaba da binciken an samu nasarar kama shugaban gungun nasu, Bello Abubakar É—an shekara 45 makaho ne wanda yake zaune a Lagos.

Shima Mukhtar Abubakar wanda yake da shekaru 59 makaho ne dake zaune a Lagos yana da mata uku da kuma Æ´aÆ´a 14 shi ne mutum na biyu da aka kama.

Mukhtar da Bello su ne suke gudanar da kasuwancin kwayar a tare yayin da mutum na uku, Akilu Amadu mai shekaru 25 wanda shima makaho ne shi ne yake bayar da kudin gudanar da kasuwancin kuma shi ne ya bawa Adamu kunshin kwayar a tashar mota.

More News

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...