Mutane 11 Sun Mutu A wani Hatsarin Mota Da Ya Rutsa Da Su A Kwara Akan Hanyarsu Ta Zuwa Lagos Daga Gombe

Akalla mutane 11 ne suka mutu wasu takwas kuma suka jikkata a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a Aiyere dake kan hanyar Bode Saadu zuwa Ilorin a karamar hukumar Moro ta jihar Kwara.

Majiyoyi sun bayyana cewa hatsarin ya faru ne 4:50 na dare sakamakon gudun ganganci da kuma kokarin wuce wata mota.

Wata mota kirar Toyota Hummer da ta taso daga jihar Gombe akan hanyarta ta zuwa Lagos ta ci karo da wata babbar mota a lokacin da take kokarin wuce wata mota.

Hukumar FRSC dake kiyaye faruwar haÉ—ura a Najeriya ta tabattar da faruwar hatsarin.

Mai magana da yawun FRSC a jihar Kwara Olayinka Bisambo ta ce ” Mutane 18 dukkansu maza hatsarin ya rutsa da su kuma abin bakin ciki 11 daga ciki sun mutu ayayin da aka ceto mutane 7 da suka samu raunuka daban.”

Ta kara da cewa an gazarzaya da wadanda suka jikkata ya zuwa asibitin Ifeoluwa dake Bode Saadu domin samun kulawar likitoci.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...