Ministan kudi ya dawo Najeriya bayan ganin likita a kasar waje

Sulaiman SaadHausa10 months ago

Wale Edun ministan kudi na Najeriya ya dawo gida Najeriya bayan da yaje wata ziyara kasar waje.

Wani fefan bidiyo da ake yaɗawa ya nuna ministan a otal din Frazer Suites dake Abuja.

An bada rahoton cewa ya yi wata ganawar sirri da wata tawagar wakilan kasar Qatar a ranar Lahadi a otal din tare da Jumoke Oduwale ministan harkokin ciniki da masana’antu da zuba jari.

A makon da ya gabata ne wasu rahotanni suka bayyana cewa ministan na fama da rashin lafiya inda ya bar Abuja a ranar Litinin ya zuwa Lagos daga can kuma ya wuce kasar waje domin samun kulawar likitoci.

A makon ne dai  mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ta tabbatar da cewa Edun ba shi da lafiya.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...