Ministan kudi ya dawo Najeriya bayan ganin likita a kasar waje

Wale Edun ministan kudi na Najeriya ya dawo gida Najeriya bayan da yaje wata ziyara kasar waje.

Wani fefan bidiyo da ake yaɗawa ya nuna ministan a otal din Frazer Suites dake Abuja.

An bada rahoton cewa ya yi wata ganawar sirri da wata tawagar wakilan kasar Qatar a ranar Lahadi a otal din tare da Jumoke Oduwale ministan harkokin ciniki da masana’antu da zuba jari.

A makon da ya gabata ne wasu rahotanni suka bayyana cewa ministan na fama da rashin lafiya inda ya bar Abuja a ranar Litinin ya zuwa Lagos daga can kuma ya wuce kasar waje domin samun kulawar likitoci.

A makon ne dai  mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ta tabbatar da cewa Edun ba shi da lafiya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]