Mayakan Boko Haram Sun Ta Da Gari A Jihar Yobe

Rahotanni daga jihar ta Yobe dai sun yi nuni da cewa wasu da ake zargin mayakan kungiyar Boko Haram ne sun kai hari a garin Babban Gida, shelkwatar karamar hukumar mulkin Tarmuwa da yammacin ranar lahadi.

To sai dai rundunar sojin saman Najeriya da ke jihar sun sami nasarar fatattakar makaran cikin daji.

Mai taimakawa shugaban karamar hukumar Tarmuwa kan harkokin yada labarai, Bulama Jalaludeen, ya tabbatar da afkuwar lamarin ta wayar tarho da safiyar yau Litinin.

Wasu majiyoyi daga yankin kuma sun yi nuni da cewa dakarun soji da ke yankin sun sami kiran gaggawa daga bisani suka kai dauki, inda suka yi musayar wuta da mayakan har suka arce daga yankin, lamarin da ya tilastawa akasarin mazauna yankin fantsama cikin dazuka don tsira da rayukansu.

A cewar Jalaludeen, mayakan sun yi ta harbe-harben bindiga kafin dakarun soji suka iso garin tare da fatattakarsu.

Wannan harin dai na zuwa ne bayan samun dan sassauci a hare-haren da ‘yan kungiyar ta Boko Haram da na ISWAP da ke mubaya’a ga ISIS ke kaiwa musamman a yankin Arewa maso gabas.

Idan ana iya tunawa a ranar 16 ga watan Satumban nan da mu ke ciki ne rundunar sojin saman Najeriya ta ce bisa kuskure wani jirgin yakinta ya bude wuta akan wasu fararen hula a kauyen Buhari da ke jihar Yobe a Arewa maso gabashin kasar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar akalla mutane 8 da jikatta wasu da dama.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...