‘Yan Sanda 17 Sun Mutu A Harin ‘Yan Ta’adda A Yobe



Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta goma sha bakwai bayan harin ‘yan ta’adda a makarantar horas da dakarun musamman ta sojoji da ke Buni Yadi a karamar hukumar Gujba ta jihar Yobe.

Mai magana da yawun rundunar, Anthony Placid, ya ce jami’an suna karbar horo na musamman ne lokacin da ‘yan ta’addan suka kai harin daga wurare daban-daban.

Ya kuma bayyana cewa wasu jami’an sojoji sun mutu yayin artabu da maharan.

Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Tunji Disu, ya bayyana mamatan a matsayin jajirtattun jami’ai da suka sadaukar da rayuwarsu wajen kare kasa.

Rundunar ta ce kwamishinan ‘yan sanda na jihar Yobe ya ziyarci cibiyar horaswar domin jajanta wa jami’an da suka tsira da iyalan wadanda suka mutu.

Haka kuma rundunar ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro domin kamo wadanda suka kai harin.

More from this stream

Recomended