Matukan jirgi biyu sun jikkata bayan da jirgin sojan saman Najeriya ya faɗo a Benue

Wani jirgin bayar da horo na rundunar sojan saman Najeriya ya fado a Makurdi babban birnin jihar Benue.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojan saman Najeriya, Edward Gbkwet ya fitar ya ce jirgin ya fado ne lokacin da ake bada horo kamar yadda aka saba yi a ko yaushe a ranar Juma’a.

Gbkwet ya ce ba a samu asarar rayuka ba amma matuka biyu dake jirgin na can na samu kulawar likitoci a asibitin rundunar sojan saman dake Makurdi bayan da suka fice ta lema daga cikin jirgin.

Sanarwar ta ce babban hafsan sojan saman Najeriya , Hassan Abubakar ya kafa kwamitin bincike da zai gano musabbabin faruwar lamarin.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...