Masu ƙwacen waya sun kashe ƴan bautar ƙasa a Kaduna

Wasu da ba a san ko su waye ba da ake zargin masu satar waya ne a ranar Laraba sun caka wa wata ƴar bautar kasa (NYSC) mai suna Chalya Silas wuka har lahira.

Rahotanni sun ce maharan sun sace wayarta kafin su gudu daga wurin.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana hakan a sakamakon yunkurin sace wayar da maharan suka yi.

Rundunar ‘yan sandan ta fara farautar wadanda ake zargin domin gurfanar da su a gaban kuliya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]