Masu ƙwacen waya sun kashe ƴan bautar ƙasa a Kaduna

Wasu da ba a san ko su waye ba da ake zargin masu satar waya ne a ranar Laraba sun caka wa wata ƴar bautar kasa (NYSC) mai suna Chalya Silas wuka har lahira.

Rahotanni sun ce maharan sun sace wayarta kafin su gudu daga wurin.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana hakan a sakamakon yunkurin sace wayar da maharan suka yi.

Rundunar ‘yan sandan ta fara farautar wadanda ake zargin domin gurfanar da su a gaban kuliya.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...