Ma’aikatan lafiya sun dakatar da yajin aikin da su ke

Sulaiman SaadHausa6 months ago

Ƙungiyar JOHESU gamayyar ma’aikatan kiwon  lafiya ta dakatar da yajin aikin da suka shafe kwanaki 84 suna yi a faɗin biyo  bayan wata yarjejeniya da su ka cimma da gwamnatin tarayya kan albashi da kuma walwalarsu.

An ɗauki matakin janye yakin aikin ne a ƙarshen taron shugabannin gudanarwar kungiyar da aka gudanar ranar Juma’a a Abuja.

Kungiyar ta ce an kira taron ne domin sake duba sakamakon da aka samu na tattaunawar sulhu tsakanin ɓangaren gwamnatin tarayya da kuma JOHESU wanda aka yi ranar Alhamis a hedkwatar ma’aikatar kwadago ta tarayya.

A wata sanarwa da aka fitar bayan taron kungiyar ta ce an dakatar da yakin aikin domin bawa gwamnati damar aiwatar da yarjejeniyar aka cimma.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...