Legas: An kama matar da ta kulle yaro a kejin kare

Wani keji

Hakkin mallakar hoto
@opetodolapo

Image caption

A daya daga cikin wadannan kejinan aka kulle yaron

‘Yan sanda a birnin Legas na Najeriya sun kama wata mata da aka dauki hotonta tana cin zarafin wani yaro sannan ta kulle shi a wani keji na karnuka.

Babu tabbas kan lokacin da aka dauki bidiyon amma an rinka yada shi a shafukan Twitter a farkon watan nan.

An ga matar a bidiyon, tana dukan yaron da bel.

Daga nan sai ta saka shi a wani keji ta rufe sannan ta kama gabanta.

Akwai wasu karnuka biyu a cikin wani keji kusa da wanda ta saka yaran.

Bidiyon ya tayar da hankulan mutane a shafukan sada zumunta, inda wasu suka yi alkawarin bayar da lada ga duk wanda ya taimaka aka gano inda matar take.

A ranar Alhamis, mai magana da yawun ‘yan sanda, Dolapo Badmos, ta wallafa a shafin Twitter cewa an kama matar.

Ta ce “Matar na hannun jami’an tsaro kuma za a gurfanar da ita a kotu… An kubutar da yaron, wanda maraya ne, kuma ana kula da shi a wani wurin mallakin gwamnatin Legas.”

Sakon da ta wallafa na dauke da shafin wani bidiyo wanda ‘yan sanda suka nada da ke nuna kejinan da aka kulle yaron:

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...