Kudu Ce Za Ta Karbi Shugabanci A 2023 – AREWA News

VOA Hausa

Gwamnonin kudancin Najeriya 17, sun cimma matsaya daya kan amincewa da mulkin karba-karba tsakanin kudu da arewa kasar, inda suka ce, su za su fitar da dan takarar shugaban kasa a zaben 2023.

Kungiyar gwamnonin ta kai ga cimma wannan matsaya ce, yayin wani taro da ta gudanar a jihar Legas a ranar Litinin.

“Kungiyar ta amince a mataki na bai daya cewa, a rika mulkin karba-karba tsakanin kudanci da arewacin Najeriya. Ta kuma amince cewa, shugaban Najeriya na gaba, ya fito daga yankin kudanci.” In ji sanarwar da kungiyar ta fitar a karshen taron wacce ke dauke da sa hannun shugaban kungiyar, gwamnan jihar Ondo, Arakunrin Oluwarotimi Odunayo Akeredolu.

Kazalika gwamnonin sun kara jaddada matsayarsu ta cewa Najeriya ta ci gaba da zama a matsayin kasa dunkulalliya bisa tsari na adalci.

Ga wasu daga cikin sauran batutuwan da taron gwamnonin kudancin na Najeriya ya cimma matsaya a kai:

– Taron ya yabawa jami’an tsaro kan namijin kokarin da suke yi wajen tabbatar da zaman lafiya tare da jajintawa iyalan jami’an tsaron kasar da suka rasa ‘yan uwansu.

– Jaddada bukatar a samar da ‘yan sandan jiha

– Taron ya amincewa a duk lokacin da jami’an tsaro za su kai wani samame a kowacce jiha, dole a rika sanar da babban mai tsaron jihar (gwamna)

– Taron bai lamunta da yadda ake nuna son kai wajen aiwatar da hukunci ba sannan ya nuna cewa a duk lokacin da za a kama wanda ake zargi da laifi, a yi hakan bisa tsarin doka da tabbatar da ‘yancin bil adama.

– Taron gwamnonin har ila yau, ya amince cewa ranar Laraba 1 ga watan Satumba, 2021 dokar haramta kiwo a fili za ta fara aiki a duk jihohin yankin kudancin kasar.

– Gwamnonin yankin ba su amince da kaso 3 da za a rika ba jihohin da ake tono arzikin mai ba, amma suna goyon bayan kashi 5 kamar yadda majalisar wakilai ta ba da shawara.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...