Kotun Koli Ta Tabbatar Da Zaɓen Gwamnan jihar Akwa Ibom

Kotun Koli ta tabbatar da Umo Eno a matsayin halastaccen zaɓaɓɓen gwamnan jihar Akwa Ibom.

Rukunin alkalan kotun su biyar ƙarƙashin jagorancin mai shari’a, Uwani Abba-Aji ta yi watsi da ɗaukaka ƙara daban-daban guda uku da jam’iyun APC da ɗantakararta, Akanimo Udofia, da YPP da ɗantararta Albert Bassey da kuma jam’iyar NNPP da ɗantararta John Udoedehe suka shigar gaban kotun.

Jagoririn lauyoyin masu shigar da kara sun janye karar ta su ne bayan da kotun ta nuna musu cewa ɗaukaka ƙarar ta su bashi da tushe balle makama.

Yan takarar sun shigar da zarge-zarge da yawa akan Eno ɗaya daga ciki shi ne cewa gwamnan ya miƙawa hukumar zaɓe ta INEC takardar kammala sakandare ta jabu.

Kotun ta nemi jin ba’asin ko masu ƙarar sun kira jami’an hukumar shiryawa jarrabawar WAEC domin su bayar da sheda kan ingancin takardar kammala makarantar.

A watan Satumba ne kotun sauraren kararrakin zabe ta tabbatar da nasarar da Eno ya samu.

Itama kotun ɗaukaka kara dake Lagos ƙarƙashin mai shari’a, Festus Obande ya tabbatar da hukuncin kotun sauraren kararrakin zaben.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...