Kotu ta samu Maman Boko Haram da aikata zamba

QBabbar kotu dake jihar Borno ta daure, Aisha Wakili wacce aka fi sani da “Maman Boko Haram” har tsawon shekaru biyar bayan da aka same ta da aikata zanba cikin aminci.

Ofishin hukumar EFCC dake yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati shiyar Borno, ya sake a gurfanar da Wakili tare da wasu mutane biyu Tahiru Daura da Prince Shoyode a cikin watan Satumba shekarar 2020 inda ake musu tuhuma biyu da suka hada da hada baki tare da karbar kudi ta hanyar zanba.

Mutanen uku sun hada baki inda suka damfari Saleh Ahmed Said na kamfanin Shuad General Enterprises bayan da suka saka ya kawo musu wake buhu 3000 da kundinsa ya kai 71,400,000 a madadin kungiyar agaji ta Complete Care and Aid Foundation.

Bayan ya kawo kayan ne sai suka bi biyansa kudinsa hakan yasa ya garzaya gaban hukumar EFCC domin neman mafita.

Mutanen za su shafe shekaru biyar da biyan tarar miliyan 30 idan kuma basu biya to za su kara shafe shekara 10 a gidan yari.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...