Kasuwar ƴan ƙwallon ƙafa: Makomar Emery, Conte, Fonseca, Xavi, Pogba, Asensio, Ibrahimovic

Antonio Conte da kofin Premier na Chelsea

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,
Antonio Conte ya daukar wa Chelsea kofin Premier a kakarsa ta farko a kungiyar a 2016-17

Newcastle ta shirya bayyana sabon mai horad da ‘yan wasanta a wannan makon, inda kociyan Villarreal kuma tsohon na Arsenal Unai Emery, mai shekara 49, ke kan gaba a yanzu. (Mirror)

Antonio Conte na shirin sanya hannu a yarjejeniyar fam miliyan 20 a matsayin kociyan Tottenham inda ‘yan wasan kungiyar ke shirin tsohon kociyan na Chelsea da Inter Milan mai shekara 52, ganin ya jagorance su a atisaye ranar Talatar nan.(Telegraph)

Tuni ma har Conten ya bukaci shugaban Tottenham Daniel Levy ya ware kusan fam miliyan 237 domin sayen wasu ‘yan wasan gasar Italiya ta Serie A, su shida da yake son daukowa. (Calciomercato, daga Express)

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,
Conte da Inter Milan sun cimma yarjejeniyar barin kungiyar bayan ya jagorance ta, ta dauki kofin Serie A na farko a shekara 11

Haka kuma kungiyar ta Tottenham na shirin biyan Nuno Espirito Santo kudin sallama da ya kai fam miliyan 14. Amma kuma da a ce an kai karshen kaka, to yarjejeniyar daukar kociyan dan Portugal ta tanadi sallamarsa ba tare da biyansa komai ba idan ba su kare gasar a cikin shidan farko ba a Premier. (Sun)

Kungiyar Al Sadd ta gaya wa jami’an Barcelona cewa lalle sai sun je Qatar idan suna son a tattauna da su domin daukar Xavi, mai shekara 41, ya zama sabon kociyan kungiyar ta Sifaniya. (AS)

Tuni Xavi ya bai wa Barcelona sunayen ‘yan wasa hudu da yake son a dauko masa, ciki har da Paul Pogba na Manchester United mai shekara 28, wanda zai kasance ba wata yarjejeniyar wata kungiya a kansa a karshen kaka. (El Nacional)

Asalin hoton, OTHERS

Bayanan hoto,
Xavi ya gabatar wa da Barcelona bukatar sayo masa Paul Pogba tun kafin ya zama kociyanta

Liverpool da Arsenal sun bi sahun Juventus da AC Milan da kuma Borussia Dortmund wajen gabatar da bukatarsu ta daukar Marco Asensio daga Real Madrid a watan Janairu, amma kuma kungiyar Jamus din ce kusan dan wasan na tsakiya dan Sifaniya mai shekara 25 ya fi so. (El Nacional )

AC Milan na shirin sake kara wa dan wasan gabanta dan Sweden Zlatan Ibrahimovic, mai shekara 40, karin kwantiragi, kamar yadda sharadin na yanzu yake. (Calciomercato)

Arsenal na duba yuwuwar dauko dan wasan gaba na Torino da Italiya Andrea Belotti, mai shekara 27. (Calciomercato)

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,
Andrea Belotti

Arsenal za ta gabatar da bukatarta ta karbar aron dan wasan gaba na Serbia Luka Jovic, mai shekara 23, daga Real Madrid. (Express)

Watakila matsi ya sa Juventus ta sayar da dan wasn tsakiya na Wales Aaron Ramsey, mai shekara 30, ko kuma Weston McKennie, na Amurka mai shekara 23, domin samun kudin sayen dan wasan gaba na Serbia Dusan Vlahovic, mai shekara 21 daga Fiorentina da kuma dan wasan tsakiya na Borussia Dortmund, dan Belgium Axel Witsel, mai shekara 32. (Tuttosport)
Paris St-Germain na neman sauya tunani a kan kwantiragin shekara biyu da t kulla da Sergio Ramos, mai shekara 35, wanda ya koma can bayan zamansa da Real Madrid ya kare watan Yuli, wanda har yanzu bai yi mata was ba saboda rauni. (Le Parisien daga AS)

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,
Tun da PSG ta dauki Sergio Ramos a watan Yuni har yanzu bai taka mata leda ba

PSG na shirin gabatar da bukatar sayen dan wasan tsakiya na Portugal Joao Palhinha, mai shekara 26, daga Sporting Lisbon. (O Jogo)

Aston Villa ta gabatar da bukatarta ga tsohon kociyan Roma Paulo Fonseca a kokarin da kungiyar take yi na neman wanda zai maye gurbin Dean Smith. (Mail)

(BBC Hausa)

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...