Kasuwar ‘yan kwallo: Makomar Rudiger da Casemiro da Hazard da Dybala da Adeyemi da Vinicius Junior da Philippe Coutinho

junior

Asalin hoton, Getty Images

Manchester City ta saka wa dan wasan tsakiyarta Phil Foden farashin fam miliyan 128, wanda hakan ya sa ya zama daya daga cikin yan wasa mafiya tsada a duniya. (Mail)

Haka kuma City na shirin bai wa mai tsaron bayanta Joao Cancelo sabon kwantiragi a farko watan Janairun 2022. (Fabrizio Romano)

Ita kuwa Liverpool ta fara sa’ido kan Raphinha na Leeds United da kuma dan wasan gaban West Ham Jarrod Bowen tun kafin watan Janairu ya kama. (Liverpool Echo)

Barcelona na duba yiwuwar yin wani garambawul da zai sa ta saka yan wasanta kasuwa, da suka hada da Frenkie de Jong, da Sergio Dest da Marc-Andre ter Stegen da Umtiti da kuma Philippe Coutinho.(Gerard Romero, via Sun)

Asalin hoton, Reuters

Borussia Dortmund ce gaba-gaba wurin son sayen dan wasan gaban Red Bull Salsburg Karim Adeyemi, wanda ake rade-radin Bayern Munich da Liverpool na nema. (Goal)

A nan kuma dan wasan gaban Real Madrid Vinicius Junior ne ya gargadi kungiyarsa cewa kar ta sa kudi kansa don bai shirya barin kungiyar ba. (Vamos, via Marca)

Manchester United na daga cikin kungiyoyin da ke sha’awar daukar Vinicius Junior daga Madrid. (Mirror)

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...