Abin da ya kamata ku sani kan wasan Man United da Man City

Solskjaer Guardiola

Asalin hoton, Getty Images

Ranar Asabar za a buga wasan hamayya tsakanin Manchester United da Manchester City a gasar Premier League a Old Trafford.

Manchester City tana ta uku a kan teburin Premier League da maki 20, ita kuwa Man United tana ta biyar da makinta 17.

Kungiyoyin sun kara sau uku a 2020/2021 da yin wasa biyu a Premier League da karawa a FA Cup.

Sun fara wasa ranar 12 ga watan Disambar 2020, inda suka tashi 0-0 a gidan United.

Sai kuma suka hadu a karawar FA Cup ranar 6 ga watan Janairun 2021, inda City ta yi nasara da ci 2-0.

A fafatawar Premier karo na biyu a kakar, United ta yi nasara da ci 2-0 a Etihad ranar 7 ga watan Maris din 2021.

United ba ta yi rashin nasara ba a wasa hudu kwanan nan a tsakaninsu a Lik, wadda ta ci wasa uku da canjaras daya.

Wasa uku kungiyar da ke gida ta yi nasara daga 16 da suka fafata a dukkan karawa a baya.

City na fatan cin wasa na takwas a gidan United, wadda ta ci shida da canjaras biyu da rashin nasara a karawa biyu

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...