Jam’iyar ADC ta kori Nafiu Bala da wasu mutane

Shugabancin jam’iyar ADC tsagin David Mark ya kori Nafiu Bala daga jam’iyar bayan da suka zarge shi a yiwa jam’iyya zango kasa.

Har ila yau jam’iyar ta kori ƙarin wasu mambobin nata ciki har da Lekan Ajibade ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Kingsley Temitope, Norman Obinna, Kennedy Odiong da kuma Stella Chukuma.

Binos Yaroe Sanata dake wakiltar mazabar kudancin jihar Adamawa shi ne ya gabatar da kudirin korar mambobin jam’iyar a ranar Talata a wurin babban taron jam’iyar a Abuja inda kuma wakilai suka amince ta hanyar kaɗa murya da bakinsu.

Da yake wa wakilan da suka halarci taron jawabi sakataren tsare-tsare na jam’iyar Chinedu Fito ne ya zargi mambobin da aka kora da yiwa jam’iyar zagon ƙasa da kuma rubuta wutar rikicin dake rarraba kan  jam’iyar.

More from this stream

Recomended