Jami’an tsaro sun dagargaji ƴan ta’adda tare da ceto waɗanda aka yi garkuwa da su a Kebbi

Dakarun runduna ta 8 ta sojojin Najeriya tare da jami’an tsaron farin kaya da na Sibil Difens da kuma ‘yan banga a safiyar Talata sun kai farmaki kan wani sansanin ‘yan ta’adda a jihar Kabbi.

Sojojin, a yayin samamen, sun kashe ɗaya daga cikin ‘yan ta’addan, tare da kubutar da mutane huɗu da aka yi garkuwa da su, tare da kwato makamai da alburusai.

Mukaddashin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojoji ta Birgediya ta 1 a Gusau Kaftin Yahya Ibrahim ne ya bayyana hakan, yana mai cewa, “An kai samamen ne a maboyar ‘yan ta’addan da ke kauyen Sabon Gari da ke karamar hukumar Shanga a Jihar Kebbi.

“A yayin farmakin, sojoji sun kashe daya daga cikin ‘yan ta’addan tare da zakulo wadanda aka yi garkuwa da su hudu.

“Sojojin sun kuma kwato bindigu kirar AK-47 guda uku, gidan alburusai uku, harsashi na musamman 142 mai tsawon milimita 7.62mm da kaki guda biyu.”

Ya kara da cewa duk wadanda aka ceto sun samu haɗuwa da dangoginsu, yayin da sojoji ke ci gaba da bin diddigin wadanda suka samu raunuka da kuma tserewa daga cikin ‘yan ta’addar.

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuɗaɗe

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...