Gwamnatin Zamfara ta fara biyan ƴan fansho haƙƙoƙinsu

Gwamnatin jihar Zamfara ta fara biyan wasu ‘yan fansho da suka yi ritaya a jihar jimillar kuɗi naira biliyan 13.4.

Ku tuna cewa gwamnatin jihar ta kafa kwamiti don tantance bayanan ma’aikatan da suka yi ritaya don biyan basussukan da aka tara daga shekarar 2011 zuwa yau.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Idris ya fitar a ranar Asabar, ya bayyana cewa wadanda suka yi ritaya suke ke bin bashin giratuti tun a shekarar 2011, daga karshe sun fara karbar kudadensu.

An fara biya tun ranar Alhamis.

“Gwamnatin jihar ta dauki wani muhimmin mataki na magance basussukan da ma’aikatan da suka yi ritaya suke bi, wanda ya hada da na mutuwa, gratuti na ritaya, da kuma na kwangila.”

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...