Gwamnatin Zamfara ta fara biyan ƴan fansho haƙƙoƙinsu

Gwamnatin jihar Zamfara ta fara biyan wasu ‘yan fansho da suka yi ritaya a jihar jimillar kuɗi naira biliyan 13.4.

Ku tuna cewa gwamnatin jihar ta kafa kwamiti don tantance bayanan ma’aikatan da suka yi ritaya don biyan basussukan da aka tara daga shekarar 2011 zuwa yau.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Idris ya fitar a ranar Asabar, ya bayyana cewa wadanda suka yi ritaya suke ke bin bashin giratuti tun a shekarar 2011, daga karshe sun fara karbar kudadensu.

An fara biya tun ranar Alhamis.

“Gwamnatin jihar ta dauki wani muhimmin mataki na magance basussukan da ma’aikatan da suka yi ritaya suke bi, wanda ya hada da na mutuwa, gratuti na ritaya, da kuma na kwangila.”

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]