Gwamnatin Legas Ta Musanta Jita-jitar Tserewar Dan Italiya

Hukumomi a jihar Legas da ke kudancin Najeriya, sun musanta rahotannin da ake yadawa ta kafofin sada zumunta cewar, dan kasar Italiyan nan mai dauke da cutar coronavirus ya tsare daga asibitin da ake kula wa da shi.

Hakan na faruwa ne yayin da gwamnati ta ce an fara gano wasu daga cikin fasinjojin da suka shiga jirgin Turkiya tare da dan kasar ta Italiya.

Mutumin dan Italiya, wanda ba a bayyana sunansa ba, na aiki ne da kamfanin siminti na Lafarge Africa Plc a jihar Ogun da ke makwabtaka da Legas.

Gwamnan jihar Ogun, yayin wani taron manema labarai na daban, ya ce, an kebe mutane 28 da ke aiki a kamfanin siminti.

Ministan lafiya, Osagie Ehanire a wani taron manema labarai a babban birnin tarayya, Abuja, a nashi bangaren ya ce hukumomin Najeriya na daukan matakan da suka dace don hana yaduwar cutar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]