Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq a ranar Litinin ya bada umarnin cewa ma’aikatan jihar su rika zuwa aiki sau uku a mako maimakon kwanaki biyar.
Shugabar ma’aikatan jihar,Susan Modupe Oluwole ita ce ta sanar da haka a Ilorin inda ta ce gwamnatin jihar ta amince da rage kwanakin a matsayin matakin wucin gadi na rage raÉ—adin cire tallafin man fetur da aka yi.
Oluwole ta gargadi ma’aikatan da kada su yi amfani da damar wajen yin sakaci da aiki.